Lyrics
Zuciya ce da numfashi
Ke amo mai zubin koke
Dake tun babu komai
Shine mafarin bayyyanar so
Toh ashe lalai ko so
Gurbi mazaunin ruhi yake kwana
Hmm-mm-mm-mm
Tafsilin so da zanyi
Akan haduwar kaunar farar ta daya
An gayyacen biki
A kace nai yo waka ta soyayya
Ina shirin na fara
Sai ga wata yarinya zubin Allah
Kirar masha Allah
Har sai dana ce subhanallah
Na tsarkake Allah
Sai tace dani
"Malam kasa min wakar izina"
Sai na fara
Izina ta
Ke nake nuni
Karka guje ni
Dan zamani
Mai kyan launi
Zan zama tsani
Samun sukuni
Taho
Taho
Izina
Nayi nuni dakai sahibi na
Kai nake so a raina
Ji tausai na, na, na
Karkato
Na mato
Ceto
Zakayi
Wakar izina har sai da ta kare
Ni da ita junan mu mun ware
Nai zaton haduwar mu ta kare
Toh ashe dai hakan ne mafari
Kuma gashi an kusa auren ta
Jini na sarauta a taken ta
Wai taya za'a faro?
Mai kallo mai sauraro
Ku biyo ni bashi na faro
Cigaban zan kwararo
Zuciya ce da numfashi
Ke amo mai zubin koke
Shi mafari na so take
Shi gamon akwai hasashe na
Lyrics powered by www.musixmatch.com